Connect with us

Labarai

Gwamna Adeleke ya kare matakinsa na yin sauyin sheka

Published

on

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya kare matakin da ya ɗauka na ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar AP, da ya ce  ya sauya sheƙa ne domin kare kan sa da kuma tabbatar da zaman lafiyar jihar.

Ta cikin wata hirar sa da  gidan talabijin na Channels a jiya  Laraba, gwamnan ya ce bai yi watsi da PDP , wacce har yanzu yake girmamawa, sai dai ya zaɓi fifita ɗorewar ci gaban da ake samu a jihar ta  Osun.

Adeleke ya shiga jam’iyyar AP ne a ranar Talatar da ta gabata  bayan ya fice daga PDP, jam’iyyar da ta bashi  mulki a zaɓen gwamnan jihar na 2022.

A ranar Laraba ne ya samu tikitin takarar gwamna a karkashin sabuwar  jam’iyyarsa ta AP, da a yanzu haka zai kara da ‘yan takara daga APC, PDP, da kuma jam’iyyar haɗaka ta ADP a wani zabe da ake sa ran zai kasance mai matukar tasiri ga makomar siyasar sa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!