Connect with us

Labarai

Gwamna Ademola Adeleke ya fice daga jam’iyyar PDP

Published

on

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya sanar da  ficewar sa daga jam’iyyar PDP, mai adawa ta kasa.

Adeleke ya sanar da hakan ne ta shafin sa na X a daren Litinin, inda ya wallafa kwafin takardar murabus dinsa mai dauke da kwanan wata 4 ga Nuwambar, 2025.

A cikin takardar, Adeleke ya bayyana rikicin da ke faruwa a jam’iyyar a matsayin dalilin ficewa rsa, da ya sa  yanke shawarar a yanzu haka.

Gwamnan ya gode wa jam’iyyar bisa damar da ta bashi ya yi aiki a matsayin Sanata mai wakiltar Osun ta Yamma wato West 2017–2019 da kuma Gwamnan jihar Osun.

Sai dai har kawo yanzu Adeleke dai bai bayyana jam’iyyar da zai koma ba bayan barin PDP.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!