Connect with us

Labarai

Gwamna Fintiri ya kai ziyarar jaje karamar hukumar Lamurde

Published

on

Gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri ya kai ziyarar jaje karamar hukumar Lamurde biyo bayan wani rikici da ya barke a tsakanin al’ummar garin.

 

Rikicin dai ya faru ne tsakanin Bachama da Chobo da ya samo asali sakamakon takaddama kan gurin noma.

 

Rikicin dai yayi sanadiyar rasa rayukan mutane shida tare da raunata wasu da dama da kone rumbuna sama da saba’in harma da lalata gidaje da sace kayan abincin mutanen yakin.

 

Da yake jawabi kan rikicin, Fintiri ya dauki matakin takaita zirga-zirga na tsawon awanni 24 tare da kai jami’an tsaro wajen da lamarin ya faru kafin daga bisani a sassauta.

 

Kana a wata ziyarar da ya kai Waduku da Lakan da kuam Rugange, gwamnan ya hore su da su rungumi zaman lafiya da kaunar juna, inda yace babu wata al’umma da zata ci gaba matukar tana fama da rikici.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!