Connect with us

Labarai

Gwamna Radda ya ziyarci garin Mantau da ƴan bindiga suka kai hari

Published

on

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya ziyarci garin Mantau da ke ƙaramar hukumar Malumfashi da ƴan bindiga suka kashe masallata domin yin ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasa ’yan uwa a harin.

Wannan na cikin sanarwar da Ibrahim Kaula Mohammed, babban sakataren yada labaran gwamnan, ya fitar ranar Laraba, 27 ga watan Agusta, 2025.

A yayin ziyarar, Gwamna Radda ya bayar da tallafin gaggawa na naira dubu dari biyar ga kowane iyali da abun ya shafa, tare da sanar da shirin gwamnati na gina makaranta da asibiti na zamani, gyaran masallaci da kuma tituna domin bada damar saurin samun taimakon tsaro.

Ya kuma bayyana cewa duk gidajen da aka lalata a harin za a sake gina su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!