Connect with us

Labarai

Za mu bai wa kowanne dan gudun hijira ɗan Borno da yake a Kamaru Naira 500,000 idan ya amince ya koma gida – Gwamna Zulum

Published

on

Gwamnatin jihar Borno ta sha alwashin inganta tsaro tare da bada kariya ga al’ummar jihar a wani mataki na kara farfado da walwalar jama’a na harkokin yau da kullum

 

Gwamnan Jihar , Farfesa Babagana Umara Zulum, ne ya bayyana hakan da ya ce gwamnatin jihar sa za ta ba kowane ɗan gudun hijira ɗan Borno da yake a Kamaru Naira 500,000 idan ya amince ya koma gida.

Zulum ya bayyana haka ne yayin da yake jawabi ga ‘yan gudun hijira a sansanin Minawao, da ke yankin Arewa ta Gabashin Kamaru.

Gwamnan ya yi wa al’ummar alkwarin samar da cikakken tsaro a yankunan da za su koma, musamman ma samarwa da jami’an tsaro abinda suke bukata da ƙarfafa tsaron farar hula a Gwoza da sauran yankuna na jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!