Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin Jigawa ta biya fiye da naira biliyan 5 hakokin ‘yan fansho

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa da hukumar kula da ‘yan fansho ta jihar sun biya fiye da Naira biliyan 5 hakokin ‘yan fansho na shekara guda.

Babban sakatare a hukumar Alhaji Ahmad Fagam ya sanar da hakan ga manema labarai a birnin Dutsen a jiya Litinin.

Alhaji Ahmad Fagam ya ce gwamnatin jihar ta ce lokaci yayi ta biya ‘yan fasnho hakokin su na shekara ta 2018 wandanda suka yi ritaya daga aiki.

Babban sakataren ya kara da cewar, hukumar ta ‘yan fasnho ta biya ‘yan fansho hakokin su na farkon watannin 6 na shekara daga watan Janairu zuwa Disamba na duk wata.

Yayi bayanin cewar kudin ya hada da wadanda suka yi ritaya da na kananan hukumomi da na kuma sashin ilimi na kananan hukumomin na jihar ta Jigawa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!