Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa ta gyara wutar lantarkin garuruwa 9 bayan lalacewar fiye da shekaru 10

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta gyara wutar lantarkin wasu garuruwa 9 bayan lalacewar da ta yi sama da shekaru 10 a yankin karamar hukumar Kirikasamma.

 

Haka kuma, gwamnatin ta kashe sama da naira miliyan dubu 30 wajen yin aiyukan hanyoyi a sassan yankin cikin shekaru biyu.

 

Gwamna Malam Umar Namadi ne dai ya bayyana haka ya yin taron gwamnati da Jama’a karo na 22 a karamar hukumar ta Kirikasamma.

 

Kananan hukumomi 5 ne dai suka rage a wannan shiri na gwamnati da Jama’a, wadda suka hada da Taura a masarautar Ringim sai ‘Yan-kwaahi a masarautar Kazaure.

 

Sauran su ne karamar hukumar Miga a Masarautar Dutse da kuma Sule-Tankarkar a yankin Gumel sai Malamadori a masarautar Hadeja.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!