Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa ta kashe sama da miliyan dubu 3 wajen samar da hasken wutar lantarki a jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta kashe sama da Naira miliyan dubu 3 wajen samar da hasken wutar lantarki a karamar hukumar Dutse, kasa da shekara guda kacal.

Da yake jawabi a gurin taron gwamnati da Jama’a karo na 9 a karamar hukumar Dutse, kwamishinan wutar lantarki Injiniya Dakta Suraja Musa ya ce daga cikin ayyukan da Sabuwar ma’aiktarsa ta yi sun hada da sabin ayyuka da gyare-gyaren kayan samar da wutar.

Kazalika Dakta Suraj ya kara da cewa birnin Dutse yafi ko ina samun aikin wuta mai yawa kasancewarta hedkwatra jihar kuma ta Karamar hukuma.

Shima  kwamishinan ayyuka da sifiri Injiniya Gambo Shuaibu Malam, ya ce nan gaba kadan gwamnatin jihar za ta fara aikin tagwayan titi zuwa Fadar mai Martaba Sarkin Dutse bayan kammala wasu sabin hanyoyin mota masu yawa birnin Dutse.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!