Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa ta sanya Naira 10,000 a matsayi Alawus ga masu Unguwanni

Published

on

Gwamnan Jihar Jigawa Malam Umar A Namadi ya amince da ƙarin alawus alawus na masu unguwanni a fadin jihar Jigawa daga naira dubu uku zuwa naira dubu goma a wata.

Hakan na zuwa ne bayan taron majalisar zartarwar jihar da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Dutse.

Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi na jihar, Dokta Nura Kazaure, ya ce ƙarin alawus ɗin na daga cikin matakan da gwamnatin jihar ke ɗauka domin nuna kulawa ga shugabannin gargajiya a matakin ƙasa, waɗanda ke taka muhimmiyar rawa wajen tafiyar da harkokin al’umma da kuma aiwatar da manufofin gwamnati.

A taron majalisar, an kuma amince da aika kudiri zuwa ga majalisar dokokin jihar ta Jigawa domin kafa Jami’ar Kimiyyar da Harkokin Lafiya, domin bunkasa fannin a fadin jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!