Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa ta yi wa Alkali Ritaya bisa samunsa da laifi

Published

on

Hukumar Kula da Ma’aikatan Shari’a ta Jihar Jigawa ta amince da yin ritayar dole ga alkalin Kotun Shari’a, Sadisu Muhammad Haruna, bisa samunsa da laifin nuna rashin da’a a aiki. 

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan yada Labarai na hukumar, Abba Wangara, ya fitar a Dutsen jihar.

Hukumar ta ce bayan nazari kan korafin da Abdullahi Hamza ya shigar da kuma hujjojin da aka gabatar, ta samu alkalin da laifin karbar kudade ba bisa ka’ida ba da kuma tsare mai kara ba bisa doka ba. 

kumar ta bayyana cewa wannan aiki na karbar kudade ta haram da kuma tsare mutum ba bisa ka’ida ba babban saba wa ka’idojin aikin shari’a ne da kuma cin zarafin mukami. 

Baya ga haka, hukumar ta kuma amince da karin girma ga ma’aikata sama da 80 a matakai daban-daban.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!