Labarai
Gwamnatin Jihar Neja ta bayar da umarnin rufe wurin haƙar ma’adanai

Gwamnatin Jihar Neja ta bayar da umarnin rufe wurin haƙar ma’adanai na Zuzungi Kataeregi da ke Karamar Hukumar Katcha na wucin gadi bayan wani rikici da ya yi sanadiyyar mutuwar jami’in tsaro.
Wannan na cikin sanarwar da Babban Sakataren Ma’aikatar Albarkatun Ma’adanai ta Jihar, Idris Legbo, ya fitar a ranar Juma’a.
Sanarwar ta bayyana cewa rikicin ya janyo lalata motar sintiri ta hadin gwiwa, lamarin da Gwamnati ta bayyana a matsayin kalubalantar ikon gwamnati da kuma halattaccen aikin hakar ma’adanai.
Rahotanni sun nuna cewa rikicin ya taso ne sakamakon takaddama tsakanin masu safarar ma’adanai ba bisa ka’ida ba da jami’an tsaro da ke aiki a wurin.
Gwamnatin ta jaddada cewa wurin na da cikakkiyar lasisi kuma yana bin dukkan tanade-tanaden doka, tare da alkawarin daukar matakan da suka dace domin dawo da zaman lafiya a yankin.
You must be logged in to post a comment Login