Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kaduna da Bankin musulunci sun gina makarantun sakandiren kimiyya da fasaha 6

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna tare da hadin gwiwar Bankin musulunci sun gina makarantun sakandiren kimiyya da fasaha guda shida kan kudi sama da naira biliyan dari bakwai da sittin da daya, domin inganta bangaren kimiyya da fasaha a jihar.

Kwamishinan ilimi na jihar Ja’afaru Sani ne ya bayyana haka, yayin wani rangadi da ya kai makarantun.

Kwamishinan ilimin ya ce kowacce mazabar Sanata, za’a gina makarantun sakandiren kimiyyar da fasaha biyu, wadanda kuma za’a wadata su da kayayyakin koyo da koyarwa na zamani, wanda zai yi daidai da tsarin horas da kimiyya da fasaha.

Ya kara da cewa makarantun ana gina su a yankunan Manchok da Jere da Buruku da Rigachukun da Pambeguwa da kuma Hunkuyi.

Sai dai yace ginin da ake yi a Manchok da Buruku da Kuma Rigachukun bai yi nisa kamar wadda ake yi a Jere ba, amma yan kwangilar da ke ginin wuraren sun ce za suyi kokarin kammalawa a kan lokaci.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!