Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

An Tashi Lafiya

Gwamnatin Kaduna ta musanta jita-jitan da ke cewa zata dakatar da layukan sadarwa a Jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna, ta sanar da cewa bata da nufin dakatar da layukan sadarwa, kamar yadda ake ta yaɗa jita-jitan cewa zata aiwatar da hakan.

Hakan ya fito ne ta bakin babban mai baiwa gwamnan Kaduna shawara a harkar yaɗa labarai Muyiwa Adekeyi, ya kuma bayyanawa Freedom Radio cewa “Gwamnatin Kaduna ba ta da nufin dakile kafar sadarwa, haka kuma ba ta sanar da yin hakan ba”.

Ya kuma ce “bamu nemi gwamnatin tarayya da ta dakatar da layukan sadarwa ba, Muna fatan al’ummar garin Kaduna za su yi watsi da waccan jita-jita, tare da cigaba da aiwatar da al’amuran su na yau da kullum ba tare da fargaba ba.

A kwana-kwanan na ne dai wasu jihohin ƙasar nan suka ɗauki sabbin matakan tsaro, wanda har ya kai ga Gwamnatin Jihar Zamfara ta dakatar da layukan sadarwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!