Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

An Tashi Lafiya

Yarima Faisal Bin Farhan ya ziyarci shugaban Najeriya

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karɓi baƙuncin Yariman ƙasar Saudiyya kuma Ministan harkokin ƙasashen waje, Yarima Faisal Bin Farhan Al-Saud a fadar sa, a ranar Talata.

Wata sanarwa da fadar ta fitar tace, Shugaba Buhari ya shaida wa Yariman cewa, Najeriya ƙasa ce mai ɗumbin jama’a kuma ga abubuwan more rayuwa, ya kuma ce ƙasar Najeriya na dogaro ne da arzikin man fetur domin samun kuɗaɗen shiga.

Shugaba Buhari, ya kuma ƙara da cewa Saudiyya na kyautata wa ƙasar nan, ta hanyar rage man da ta ke siyarwa ƙasar nan a lokuta da dama.

Shi ma Yarima Al-Saud, ya miƙa saƙon gaisuwar Sarki Salman bin Abdulaziz Al-Saud ga Buhari, yana mai cewa “Saudiyya ta yaba da alaƙarta da Najeriya ta tsawon shekara 61 kenan, kuma tana fatan ɗorewar ta.” kamar yadda BBC suka rawaito.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!