Labarai
Gwamnatin Kano ta bawa mazauna Tal’udu da Sani Mainagge wa’adin tashi domin fara aikin Gada bayan biyan su haƙƙokin su.

Gwamnatin jihar Kano ta bai wa al’ummar Unguwannin Tal’udu da Sani Mainagge da Kabuga waɗanda aikin Gadar Sama ya shafi gidajensu wa’adin fara kwashe kayansu domin fara aiki.
Daraktan harkokin kuɗi da mulki na ma’aikatar kasa daya wakilci kwamishan, Alhaji Hamid Sidi Ali ya ce a yanzu haka gwamnatin Kano ta biya diyyar gidajen da aikin gadar ya shafa dan haka gwamati take kira ga masu gidajen dasu fara haɗa kayayyakinsu kafin fara wannan aiki.
Muhammad Yahuzu babban sakatare a ma’aikatar kasa ya ce Gwamnatin Kano ta samar da matakan tsaro domin fara wannan aiki .
Shugaban kungiyar wadanda aikin ya shafa Alhaji Abba Aminu Imam ya godewa Gwamnan Kano Alh Abba Kabir Yusuf bisa cika alkawari da yayi na basu diyya mai kyau ta gidajensu tare da basu filotai a wasu mahimman wurare.
You must be logged in to post a comment Login