Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano ta kuduri sabunta ginin Majalisar dokoki da gina Titina

Published

on

Gwamnatin jihar Kano, bayyana shirinta na fara gudanar da aikin sabunta ginin zauren majalisar dokoki da kuma wasu ayyukan samar da titi mai tsawon kilomita Ashirin a karamar hukumar Makoda da wasu titunan a cikin kwaryar Birni.

 

Kwamishinan ayyuka da gidaje injiniya Marwan Ahmad, ne ya bayyana hakan, ta bakin Daraktan tsare-tsare da bincike na ma’aikatar ayyuka  Injiniya Lawal Datti a zantawarsa da manema labarai jim kadan bayan taron ganawa da yan kwalgilar da ke takarar neman yin ayyukan.

 

Daya daga cikin masu neman Kwangilar ayyukan Garzali Muhammad Usman, wanda yayi magana a madadin sauran ‘yan kwangilar, ya bada tabbacin yin aiki mai inganci domin ci gaban al’ummar jihar Kano.

 

Ma’aikatar ayyukan, ta bukaci wadanda za su rabauta da kwangilar da su tabbatar sun yi aiki mai inganci kuma a kan lokaci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!