Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano za ta dauki matakan doka kan masu gini ko zuba Shara a magudanar ruwa

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano zata dauki matakan doka kan masu gini ko zuba Shara a magudanar ruwa dake jawo ambaliyar a birni da wajen Jihar.

Kwamishinan ma’aikatar Muhalli da sauyin yanayi na Jihar Kano Dahiru Muhammad Hashim ne ya bayana hakan da safiyar yau Jumma’a lokacin da yake kaddamar da Shirin yashe magudanan ruwa a shataletalen Baban Gwari dake nan Kano.

Dahiru Hashim, ya Kara da cewar kaddamar da yashe magudanan ruwa na cikin matakan kare ambaliyar ruwa da hukumar yanayi tayi hasashen samu a jihohin kasar nan ciki hadda Jihar Kano.

Ma’aikatar ta kuma bukaci sauran mazauna unguwanni su tabbatar da gyaran magudanan ruwansu kafin faruwar damuna Dan kaucewa ambaliya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!