Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Neja ta bukaci wanda sukayi gini akan hanyar ruwa da su tashi

Published

on

Gwamnatin jihar Neja ta bukaci mazauna yankunan da suka gina gidaje a kan magudanan ruwa da su yi gaggawar tashi don kaucewa ambaliyar ruwa.

Mataimakin gwamnan jihar Yakubu Garba ne ya ba da umarnin a jiya Laraba yayin ziyarar duba wasu yankuna da ambaliyar ruwa ta shafa, biyo bayan mamakon ruwan sama da aka a kwanakin baya a jihar.

Ya kuma umarci hukumar raya birane ta jihar da hukumar bada agajin gaggawa NSEMA da hukumar kare muhalli NISEPA da su wayar da kan jama’ar da ke zaune a magudanan ruwan kan illar da ke tattare hakan.

Rahoton: Abdulkadir Yusuf Gwarzo

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!