Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Taraba ta haramta hawa Babura a Jalingo

Published

on

Gwamnatin jihar Taraba, ta sanar da haramta amfani da babura kowane iri a Jalingo, babban birnin jihar.

Haka kuma, gwamatin ta sanya dokar takaita zirga-zirgar Babura masu kafa uku watau Adaidaita sahu daga karfe 6:00 na safe zuwa karfe 8:00 na dare.

Wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar ya fitar, ta ce an ɗauki matakin ne sakamakon ƙaruwar ayyukan ta’addanci a kwaryar birnin Jalingo.
Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnatin jihar ta kafa wani kwamiti karkashin jagorancin kwamishina ƴan sandan jihar domin tabbatar da haramcin ya yi aiki kamar yadda ya kamata.
Gwamnatin ta ɗau alwashin kama wa da kuma hukunta waɗanda suka bijire wa haramcin hawa baburan, inda ta ce za a kwace babura da adai-daita sahun da suka saɓa dokar sannan a lalata su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!