Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin Taraba ta musanta zargin sayan makamai

Published

on

Gwamnatin jihar Taraba ta musanta zargin cewa ta siyo makamai ta rabawa kungiyoyin sakai don farwa Fulani makiyaya a kokarin da take na kaddamar da dokar haramta kiyo a fadin jihar.

Gwamnan jihar Darius Ishaku ne ya bayyana hakan yau, a wani mataki na martani kan zargin da wani marubuci Dr. Aliyu Tilde yayi wa gwamnatin, inda yace gwamnatin jihar Taraba na shirye-shiryen zubar da jinin Fulani a jihar ta hanyar kirkiro da dokar haramta kiwo wacce zata fara aiki kwanan-nan.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun gwamnan Emmanuel Bello.

Sanarwar ta ce, babu kanshin gaskiya cikin zargin kuma babu wani lokaci da jihar ta sayo makamai domin rabawa ga matasa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!