Connect with us

Labarai

Gwamnatin Taraba ta raba tallafi ga mutanen da rikicin manoma da makiyaya ya shafa

Published

on

Gwamnatin jihar Taraba, ta raba tallafi ga mutanen yankunan da rikicin manoma da makiyaya ya shafa a Karamar Hukumar Karim Lamido, domin farfaɗo da rayuwar jama’a da rage musu radadin halin da suke ciki.

 

Wannan na cikin wata sanarwa da Gwamnatin ta fitar ta na mai cewa, kayayyakin da aka raba din sun haɗa da hatsi da taki  da kananan injinan noman zamani don ƙarfafa aikin noma da bunƙasa amfanin gona a yankin.

 

Mutanen yankunan da suka amfana sun haɗa da Munga Lelau da Munga Dosso da Ngorore Jabu duk a Karamar Hukumar Karim Lamido.

 

Gwamnan jihar Agbu Kefas ya bayyana cewa gwamnati na ƙoƙarin samar da tsaro da yanayi mai kyau da zai bai wa jama’a damar komawa gidajensu su ci gaba da noma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!