Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya na da kudurin tallafa wa marasa karfi- Minista Doro

Published

on

Gwamnatin Tarayya, ta tabbatar wa da mutanen da ke cikin mawuyacin hali cewa, ta na da cikakken kudiri na taimaka musu da kuma tabbatar da tsaron rayukan su.

Ministan jin kai da rage talauci Bernard Doro, ne ya bayyana hakan  yayin da yake zantawa da manema labarai a Jos babban birnin jihar Plateau  a ranar Litinin, Da  ya ce manufar ma’aikatarsa ita ce tabbatar da cikar buri ga talakawa, masu gudun hijira, da sauran marasa galihu.

A cewarsa, ma’aikatar za ta inganta tsarin tallafi, fadada damar samun shirye-shiryen rage talauci, tare da tabbatar da cewa taimakon jin kai yana isa ga wadanda suka fi bukatar sa.

Ministan ya kara da cewa gwamnati za ta aiwatar da ayyukan jin kai ba a matsayin taimako ba, sai a matsayin hakkin da gwamnati ke da shi ga ‘yan Nijeriya, domin tabbatar da abinci, ilimi, da mafaka ga marasa karfi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!