Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ayyana Juma’a a matsayin ranar hutun ma’aikata

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a 1 ga watan Oktoba a matsayin ranar hutu ga ma’aikata.

Hutun wani ɓangare ne na murnar cikar Najeriya shekaru 61 da samun ‘yancin kai.

Ministan cikin gida Rauf Aregbesola ne ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya.

A cikin wata sanarwa da Dr Shuaib Belgore, babban sakataren ma’aikatar ya fitar na bayyana cewa minista Rauf ya taya dukkanin ƴan Najeriya murnar bikin zagayowar shekarar tare da ba da tabbacin jajircewar gwamnati na magance duk wasu ƙalubale.

Rauf Aregbesola ya yi kira ga ƴan Najeriya da su hada hannu da gwamnati don tabbatar da samun ci gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!