Connect with us

Kasuwanci

Gwamnatin tarayya ta bayyana alhini bisa fashewar tankar dakon Mai a Neja

Published

on

Gwamnatin tarayya ta bayyana alhininta dangane da fashewar wata tankar man fetur a garin Essa da ke karamar hukumar Katcha a jihar Neja, da ta yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu.

Ta cikin  sanarwar  da ya raba wa manema labarai a jiya  Laraba birnin tarayya  Abuja, Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici tare da mika ta’aziyya ga gwamnati ga iyalan wadanda abin ya shafa da kuma al’ummar jihar Neja.

Haka zalika Gwamnatin Tarayyar  ta koka da cewa, duk da wayar da kan jama’a da kuma gargadin da ake ci gaba da yi, har yanzu  mutane  suna kasada da rayukansu, ta hanyar  ɗibar mai yayin da tankunan dakon sa  suka faɗi.

Mohammed Idris, ya ce tuni an umarci Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa NEMA,  da ta hada karfi da  Gwamnatin Jihar ta hanyar samar da kayan agaji da taimakon magunguna ga wadanda abin ya shafa da iyalan su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!