Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya ta bayyana damuwa bisa matakin da ASUU ta ɗauka

Published

on

Gwamnatin Tarayya ta nuna damuwarta kan matakin da ƙungiyar malaman jami’o’i ASUU, ta ɗauka na tafiya yajin aiki, inda ta bayyana cewa bai kamata su tafi ba, alhalin ana tsaka da tattaunawa.

 

Gwamnatin, ta bakin Ministan Ilimi, Dakta Maruf Tunji Alausa ta ce bai kamata ƙungiyar malaman jami’o’i ta ƙasa, ASUU, ta fara raba goron gaiyatar tafiya yajin aiki ba tunda ana tattaunawa da duk kungiyoyin da abin ya shafa.

 

Ya ce gwamnatin taraiya na iya bakin kokarin ta na gyaran makarantun gaba da sakandire a fadin ƙasar nan.

 

Jaridar The Nation ta rawaito cewa Alausa ya roƙi ƙungiyoyin da ke shirin tafiya yajin aikin da su dakatar da shirin su tunda gwamnati na tattaunawa da su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!