Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya ta ce al’umma su zama cikin shirin cutar Sankarau

Published

on

Gwamnatin tarayya ta bukaci al’ummar kasar nan su zama cikin shiri tare da sanar da hukumomi da zarar sun ji inda cutar Sankarau ta bulla, kasancewar karatowar lokacin barkewar cutar.

Ministan Lafiya Farfesa Isaac Adewole ne ya yi wannan kira a garin Badin na Jihar Oyo a karshen makon da ya gabata, lokacin da ya ke gabatar da jawabi ga manema labarai na fannin kiwon lafiya, dangane da shirye-shiryen da ma’aikatarsa ke yi wajen shawo kan wannan matsala da cutar Sankarau.

Ministen ya nanata bukatar ankarar da hukumomi cikin lokaci matukar aka samu barkewar cutar, kasancewar kasar nan ba ta da wadatattun kudin da za ta yi wa dukkannin al’ummar kasar Rigakafin cutar.

Farfesa Isacc Adewole ya buga misali da Jihar Kaduna sai dai da ya ke an dauki matakin gaggawa hakan ya sa aka shawo kan cutar cikin lokaci, amma ko da aka samu irin hakan a Jihar Zamfara mutane da dama ne suka rasa rayukansu sakamakon gaza sanar da hukumomi cikin lokaci, kuma aka gaza daukar matakan gaggawa a kai a shekarar da ta gabata.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!