Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya ta ce ta biya kimanin fiye da dala biliyan 5 ga jihohin kasar nan a rarar Paris club

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce ta biya kimanin dala biliyan 5 da miliyan dari hudu ga jihohin kasar nan a wani bangare na rarar Paris Club.

Minister kudi Zainab Ahmad ce ta tabbatar da baiwa gwamnonin kudin a yau Litinin a birnin tarayya Abuja.

Minstar ta ce adadin kudaden da aka baiwa jihohin idan aka juya su a kudaden Najeriya sun kai sama da tiriliyan daya da rabi, inda kuma ta ce an baiwa jihohin kudaden ne akan sharadi.

Wasu daga cikin sharudan sun hadar da, dole ne jihohi su biya albashi a karshen kowanne wata, kuma dole ne jihohi su biya kudaden da suka ara suka cike gibin kasafin kudi a shekarar 2016

Sauran sharuddan sun hadar da biyan Kason su ga hukumar ilimin bai daya ta kasa inda ita ma gwamnatin tarayya za ta bada nata kaso domin bunkasa bagaren ilimin firamare a kasar nan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!