Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da cibiyoyin tattara bayanai a jihar Zamfara

Published

on

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da cibiyoyin tattara bayanai da zasu taimaka wajen samar da bayanai na yaki da ‘yan ta’adda a fadin jihar Zamfara.

Ministan sadarwa da bunkasa fasahar zamani na kasa Dr Isa Ali Ibrahim Pantami, ne ya bayyana haka a lokacin da ya gana da gwamman jihar Zamfara Muhammad Bello Matawalle a birni tarayya Abuja, kamar yadda sanarwar da mai magana da yawun ministan Uwa Suleiman, ya bayyana.

Dr Isa Ali Pantami, ya ce cibiyoyin zasu fara aiki a watan Agusta mai kamawa domin tababatar da an samu bayanai da zasu rinka taimakawa hukumomi da jami’an tsaron kasar nan a kokarin da ake na yaki da ‘yan ta’adda.

A nasa jawabin gwamna Bello Matawalle, yace samar da sabon tsarin zai taimaka wajwen cike gidin da aka samu a baya na musamman ma na kyale kamfanonin sadarwa suna gudanar da aiyyukan su ba tare da tantance matsaloli da masu aikata laifi keyi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!