Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An binne marigayi tsohon shugaban kasar Zambia

Published

on

An kammala jana’izar tsohon shugaban kasar Zambia wanda ya jagoranci karbo ‘yancin kasar, Kenneth Kaunda inda aka birne shi a makabartar da ake binne manyan shugabannin kasar duk da kin amincewar hakan daga ‘yan uwansa.

Gabanin fara jana’izar alkalin babbar kotun kasar, Wilfred Muma ya ki amincewa da bukatar a birne shi a gonarsa, ya na mai cewa Kaunda na daga cikin muhimman mutanen da ake alfahari da su a kasar, don haka za a binne shi a inda ya dace.

Hakan ta sanya gwamnatin kasar ta bayar da umarnin gudanar da bikin jana’izar a Embassy Park, wata makabarta ta alfarma da aka kebewa shugabannin kasar.

Wasu daga cikin dangin marigayin dai sun so a binne shi a wata gonarsa kusa da inda aka birne matarsa Betty.

Dubban mutane ne a kasar ke bayyana alhinin mutuwar Kaunda da ya koma ga mahaliccinsa yana da shekaru 97 a Duniya, wadanda ke bayyana shi a matsayin mai fafutuka dan gwagwarmaya kuma malami wanda ya kamata ayi koyi da shi.

Shugaba Edgar Lungu ya bayyana ranar haihuwar Kaunda, 28 ga Afrilu, a matsayin ranar hutu don girmama shugaban kasar na farko kuma dan fafatuka wanda ya yi gwagwarmayar kwato ‘yancin kasar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!