Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin tarayya ta kashe dala biliyan tara wajen gudanar da ayyukan raya kasa

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce cikin shekaru uku da suka gabata ta kashe dala biliyan tara wajen gudanar da ayyukan raya kasa.

 

Ministan yada labarai da raya al’adu Alhaji Lai Muhammed ne ya bayyana haka, yayin wani taron manema labarai, a wani bangare na shirye-shiryen fara taron hukumar kula da yawon bude ido na majalisar dinkin duniya shiyyar afurka karo na sittin da daya wanda za a fara yau a Abuja.

 

Ya ce gwamnati ta fi ba da fifiko wajen gyara tituna da shimfida layin dogo da gyaran filayen jiragen sama domin da cewa da zamani.

 

A cewar Alhaji Lai Muhammed, wasu daga cikin kudaden an kashe su ne ta hanyoyin bunkasa harkar bude ido wanda ya ce zai taimaka gaya wajen samar da kudade ga kasar nan.

 

Alhaji Lai Muhammed ya kara da cewa, ana saran wakilai dari da sittin da shida daga kasashe daban-daban da ministoci ashirin da shida da kuma wakilai dari uku da talatin da biyu daga kasar nan ne za su halarci taron.

 

 

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!