Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Najeriya na kashe naira biliyan 60 wajen gyaran bututun man fetur a duk shekara – Lai Muhammad

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce a duk shekara tana kashe kudi naira biliyan sittin don gyaran bututan man fetur din da bata-gari suke lalatawa a kasar nan.

Ministan yada labarai da al’adu Alhaji Lai Muhammad ne ya sanar da hakan a Abuja lokacin taron masu ruwa da tsaki kan harkokin man fetur da iskar gas, wanda aka gudanar a Abuja.

Lai Muhammad, ya ce, a duk shekara Najeriya tana asarar gangar mai dubu dari biyu a dalilin fasa bututun mai da bata-gari ke yi.

Ya kara da cewa daga watan Janairun shekarar 2019 zuwa Satumbar 2020, an lalata bututan mai guda dubu daya da dari daya da sittin da daya a Najeriya.

A na sa jawabin, ministan kula da harkokin yankin Neja-Delta Godswill Akpabio, ya ce masu zuba jari na kasashen waje da dama ne suka fice daga yankin sakamakon ayyukan tsagerun Neja-Delta.

Shi kuwa ministan muhalli Muhammad Mahmoud Abubakar cewa ya yi Najeriya tana asarar kashi 43 cikin 100 na kudaden shiga na mai sakamakon sace man da tsagerun Neja-Delta ke yi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!