Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya ta magantu kan zargin El-rufa’i

Published

on

Ofishin Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, ya karyata zargin tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, na cewa gwamnati na biyan kuɗin fansa ga ’yan bindiga.

 

Sanarwar ta ce, gwamnati ba ta taɓa biya ko bayar da wani abu ga ’yan ta’adda ba, sai ma gargadin da ta sha yi ga yan ƙasa da su guji yin hakan.

 

Gwamnatin ta bayyana cewa, rundunonin tsaro sun yi nasarar fatattakar yan bindiga a Kaduna, inda aka kashe tare da kama shugabanninsu da dama, abin da ya kawo aka samu zaman lafiya a yankin.

 

Ta ƙara da cewa waɗannan nasarori sun samu ne sakamakon sadaukarwar jami’an tsaro, don haka yin watsi da ƙoƙarinsu ba daidai ba ne.

 

Haka kuma gwamnatin ta roƙi yan siyasa da su guji mayar da batun tsaro siyasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!