Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatoci ba su da iko kan titinan gwamnatin tarayya – Gbajabiamila

Published

on

Shugaban majalisar wakilai Femi Gbajabiamila ya ce ba abu ne mai yuwa ba, jihohin kasar nan su karbi jan ragamar kula da titina mallakin gwamnatin tarayya har sai an yi wa dokar da ta ba su iko gyaran fuska.

Femi Gbajabiamila ya bayyana hakan ne jim kadan bayan ganawa da gwamnan jihar Ogun Dapo Abiodun a birnin Abeokuta a jiya Laraba.

Shugaban majalisar wakilan wanda ya bayyana yadda lalacewar hanyar zuwa manyan masana’antu a jihar ya yi da abun takaici, yana mai cewar majalisar zata yi duk mai yuwa wajen an inganta hanyoyin jiha da samar da ababan more rayuwa.

Da yake bayani gwamnan jihar Dapo Abiodun y ace yana shawartar gwamnatin tarayya ta mallakawa jihohi wasu titina don samun saukin gyara su bayan da suka lalace.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!