Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwmantain tarayya ta bukaci dakatar da dokar haramta kiwo barkatai

Published

on

Gwamnatin tarayya ta bukaci da a dakatar da dokar nan da ta haramta yin  kiwo barkatai da wasu jihohin kasar nan suka kafa.

 

Ministan tsaro Burgediya Janar Mansur Dan-Ali mai ritaya ne ya bayyana haka jim kadan bayan kammala wani taron sirri da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gudanar a fadar Asorok da ke Abuja.

 

A cewar sa dakatar da dokar a yanzu za ta taimaka gaya wajen dakile wasu matsalolin tsaro da ke addabar kasar nan.

 

Ministan ya kuma bukaci jami’an tsaro da su gaggauta gurfanar da wadanda aka kama suna da hannu cikin rikicin da ke faruwa tsakanin makiyaya da manoma gaban kotu.

 

Da yammacin jiya ne dai shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi wani taron sirri da shugabannin hukumomin tsaron kasar nan a fadar Asorok.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!