Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hajjin Bana: Akwai yiwuwar samun karin farashin kuɗin aikin Hajji- NAHCON

Published

on

Hukumar kula da aikin hajji ta ƙasa NAHCON ta ce, akwai yiwuwar samun karin farashin kuɗin aikin Hajji a bana.

A cewar NAHCON hakan ya biyo bayan karin kudin masaukin alhazai da hukumomin ƙasar Saudiyya suka yi.

Rahotanni sun nuna cewa ƙasar Saudiyya ta rushe wasu daga cikin masaukan da alhazai ke sauka domin kawatasu da hakan ka iya shafar farashin masaukin da alhazan za su sauka a bana.

Cikin jihohin da abin zai fi shafa sun haɗa da Kano, Sokoto, Katsina, Kaduna, Bauchi, Kwara, Plateau.

A bana dai ana sa ran maniyyata daga Najeriya sama da miliyan 3 ne za su sauke farali, adadin da ya fi na shekarar 2022.

Da yake ƙarin haske kan lamarin Kwamishinan hukumar NAHCON mai kula da harkokin kudi da ma’aikata Alhaji Nura Hassan Yakasai, tabbatar da cewar cewa tuni tawagar su ta isa ƙasar Saudiyya don tattaunawa da mahukunta.

A cewar sa “Za mu tabbatar da alhazan Najeriya sun samu sassaucin farashi da masauki mai arha a hajjin bana”.

Sai dai ya buƙaci maniyyata aikin Hajjin bana da su yi shiri a kan lokaci don gujeea fuskantar ƙalubale.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!