Connect with us

Kasuwanci

Har yanzu muna kan bakanmu na yajin aiki- NUPENG

Published

on

Kungiyar Ma’aikatan dakon Man Fetur da Iskar Gas ta Najeriya NUPENG, ta ce za ta ci gaba da yin yajin aiki a fadin kasar biyo bayan gaza cimma matsaya da gwamnatin tarayya kan dakon man fetur da kamfanin Dangote zai fara zuwa gidajen Mai.

 

Shugaban NUPENG, Williams Akporeha, ya bayyana hakan a zantawarsa da tashar Talabijin ta Arise.

 

Taron da Ministan Kwadago da Ayyuka, Muhammad Dingyadi, ya jagoranta a jiya Litinin ya ƙare ba tare da nasara ba, sakamakon rashin jituwa kan batun kafa ƙungiyar direbobin tankuna a masana’antar ta Dangote.

 

Ya kuma ce ƙungiyar ba ta da wata mafita illa ta ci gaba da yajin aiki, bayan da ya zargi shugabancin Dangote da ƙin amincewa da ƙungiyoyin kwadago na man fetur, tare da ƙirƙirar wata ƙungiya ta daban ga ma’aikatansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!