Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Harin da aka kai wa gwamna Zulum ya yi sanadiyyar mutuwar sojoji 4 da ‘yan sanda 10

Published

on

Rundunar sojin kasar nan ta sanar da cewa jami’anta hudu da kuma ‘yan sanda goma aka kashe yayin kwanton bauna da ‘yan kungiyar Boko Haram suka yi tawagar gwamnan Jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum a ranar juma’ar da ta gabata.

Wata sanarwa da babban jami’in yada labaran rundunar tsaro ta kasa Manjo Janar John Enenche ya fitar, ta ce sun gano gawarwakin jami’an na su a daji ne sa’o’i 24 bayan harin da aka kaiwa jerin gwanon motocin gwamnan a kauyen Barwati a kan hanyarsu ta zuwa garin Baga.

Sanarwar ta kara da cewa tuni suka aike da kararrun jami’ansu masu gano inda aka binne nakiyoyi da sauran abubuwa masu fashewa domin kawar da su.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!