Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

FRSC ta kama masu karya dokokin tuki 262 a jihar Kaduna

Published

on

Hukumar kiyaye afkuwar hadura ta kasa FRSC reshen jihar Kaduna ta ce ta gurfanar da wadanda suka karya dokokin tuki su akalla dari biyu da sittin da biyu a jihar, daga watan Janairu zuwa Agustan da ya gabata.

Babban kwamandan hukumar mai kula da shiyyar Kaduna Hafiz Muhammad ne ya bayyana hakan a yau.

Ya ce kotunan tafi-da-gidanka da hukumar ta samar guda bakwai sun kama mutane da laifuka da dama na karya ka’idojin hanya yayin da tuni ta sallami mutane goma sha tara.

Hafiz Muhammad ya kara da cewa mutane 75 aka kama da laifin rashin lasisin tuki yayin da mutana 48 kuma aka kama su da laifin dibar kaya fice da kima, sai mutane 42 da aka kama da laifin rashin madaurin direba wata seat belt.

Hka zalika mutane 39 sun aikata laifin gudun wuce sa’a sai kuma mutane 30 da suka aikata laifin yin tuki ba tare da abin goge gilashi yayin da ake ruwa.

Hafiz Muhammad ya ja hankalin direbobi da su guji karya dokokin tuki, inda ya bukaci fasinjoji da su kiyaye baiwa masu ababen hawa damar dibar kaya da suka wuce ka’ida.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!