Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zamu yi aiki tare da hukumar kiyaye hadura ta kasa dake Kano- Haroun Ibini Sina

Published

on

Hukumar Hisbah ta  jihar Kano ta kai ziyara ga hukumar kiyaye afkuwar hadura ta kasa a jiya Laraba

Babban kwamandan hukumar Hisbah Sheikh Muhammad Haroun Ibini Sina ne ya jagoranci tawagar hukumar Hisba don kai ziyarar.

Kazalika hukumnar ta Hisba ta nemi hadin kai domin yin aiki tare da jami’an hukumar kiyaye afkuwar haduran don ciyar da al’ummar jihar Kano gaba.

Da yake jawabi shugaban hukumar kiyaye afkuwar hadura ta kasa shiyyar Kano Zubairu Mato wanda ya karbi tawagar ta hukumar Hisbar ya nuna farin cikin matuka da wannan ziyara aiki.

Har ila yau Zubairu Mato yayi alkawarin cewa hukumar su zata yi aiki kafada-da-kafada da hukumar Hisbah musamman wajen lura da sanya idanu ga masu amfani da ababan hawa domin tabbatar da zaman lafiya ga al’umma baki daya.

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!