Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar JAMB ta ce ta shirya tsaf don fito da bayyanan yadda ta kashe kudadenta

Published

on

Hukumar shirya jarabawar shiga manyan makarantu ta kasa JAMB ta ce ta shirya tsaf don fara fitar da kundin bayanan yadda ta ke kashe kudaden ta, don kauda shakku a zukatan al’umma da kuma fito da komai fili.

Shugaban sashen yada labarai na hukumar Dr. Febian Benjamin ne ya bayyana hakan a yayin da yake tattaunawa da manema labarai a yau litinin a jihar Lagos.

Benjamin yace za’a rika wallafa kundin, wanda aka yiwa suna da Jambulletin duk ranar litinin, inda yace ba sayarwa za’a rika yi ba.

Ya kuma kara da cewa hukumar zata fara sayar da fam na rubuta jarabawar ta JAMB ta shekarar 2019 a ranar 10 ga watan janairun da muke ciki.

Sannan ya kuma ce ba wai iya batutuwan kudi kadai kundin zai kunsa ba, har ma da bayanan nasarorin da hukumar ta ke samu da kuma yadda ta ke gudanar da ayyukan ta don amfanin al’umma.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!