Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Fadar shugaban kasa ta musanta umarnin kama Amaju Pinnick

Published

on

Fadar shugaban kasa ta musanta batun da ke yawo cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada Umarnin kamawa tare da gurfanar da shugaban hukumar kwallon kafa ta kasa Amaju Pinnick.

Rahotanni sun bayyana cewa fiye da sa’o’I 24 kenan da labarin ya fara yawo cewa akwai babbar barazana da ke fuskantar hukumar ta kwallon kafa, inda ake yadawa cewa shugaban Buhari ya bada umarnin chafkewa da kuma gurfanar da shi gaban kotu kan zargin cin hanci da rashawa.

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimakin shugaban kasa kan harkokin yada labarai malam Garba Shehu, ya fitar a Abuja ta bayyana cewa wannan labari bashi da tushe ballantana makama.

Garba Shehu ya kuma ce duk wanda ya san shugaba Buhari ya sanshi da bin doka da oda, adon haka babu yadda za’a yi shugaba Buhari ya dauki wannan mataki kai tsaye.

Daga nan kuma sai ya yi kira ga al’umma da su yi watsi da wannan batu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!