Connect with us

Labarai

Hukumar jin dadin Alhazai ta Kano ta fara yi wa maniyyata allurar riga-kafi

Published

on

Hukumar jin dadin Alhazai ta jihar Kano, ta fara yi wa maniyyata aikin hajjin bana allurar rigakafi da kuma duba lafiyar su.

Shugaban hukumar Alhaji Lamin Rabi’u Danbaffa, ne ya kaddamar da fara aikin riga-kafi da duba lafiyar maniyyatan.

Da ya ke jawabi yayin kaddamarwar, Alhaji Lamin Danbaffa, ya kara da cewa hakan na daga cikin manyan shirye-shiryen da suka kamata hukumar ta yi domin kauce wa samun matsalar rashin lafiya lokacin tafiya ibadar

Da take jawabi, jami’ar kula da lafiya ta hukumar jin dadin Alhazai ta Kano Hajiya Hindatu Mukhtar ta ce, an tanadi dukkan kayayyakin aikin da suka dace domin tabbatar da cewa kowanne maniyyaci ya samu allurar rigakafinsa a lokacin da ya dace.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!