Connect with us

Labarai

Hukumar NiDCON ta karbi mutane 13 da aka yi safararsu zuwa Ghana da Mali

Published

on

Hukumar kula da yan Najeriya mazauna kasashen ketare NiDCON, ta karbi wasu mutane 13 da aka yi safararsu zuwa kasashen Ghana da Mali.

 

Shugabar hukumar Abike Dabiri-Erewa, ce ta tarbi wadanda aka dawo da su din da suka hada da ‘yan mata 12 da karamin yaro 1 dan shekara biyar.

 

Ta cikin sanarwar da hukumar ta fitar ta ce, daga cikin ‘yan matan da aka ceto din sun bayyana cewa an yaudare su  ne tare da tilasta musu shiga munanan ayyuka bayan an ce za a sama musu aiki a Ghana da Mali.

 

Haka kuma, yan  matan sun kara da cewa, waɗanda suka yi safarar su din suna  cin zarafin su. 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!