Connect with us

Labarai

Hukumar NiMet ta fitar da sabon hasashen yanayin da za a fuskanta

Published

on

Hukumar kula da harkokin yanayi ta Najeriya NiMet, ta yi hasashen cewa za a samu ruwan sama hade da tsawa a sassa daban-daban na kasar daga yau  Talata zuwa Alhamis mai zuwa.

Hasashen wanda hukumar ta fitar a baya bayan nan a birnin tarayya Abuja,  ya ce akwai yiwuwar  cewa za a fuskanci hadari hade da walkiya da tsawa a jihohin Katsina da Kano a yau Talata.

Rahoton ya kuma bayyana cewa, akwai yiwuwar samun hadari da tsawa mai karfi a jihohin Taraba da Adamawa da kuma zafin rana, yayin da  yankin Arewa ta Tsakiya, ake sa ran sararin samaniya za ta kasance da hadari kadan tare da walkiya da tsawa a Nasarawa da Kogi da Kwara, sai Benue da kuma birnin tarayya Abuja.

Hukumar ta Nimet , ta kara da cewa a yankin Kudu kuwa, hasashen ya nuna za a samu saukar ruwa, sannan tsawa ta biyo baya a jihohin Akwa Ibom da Cross River, sai Rivers da kuma Bayelsa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!