Labarai
Hukumar NiMET ta fitar da sabon rahoton yanayi

Hukumar kula da yanayi ta kasa NiMET ta ce jihohin Arewa za su fuskanci yanayin hazo da iska na tsawon kwanaki uku daga yau Litinin zuwa Laraba.
Hakan na cikin rahoton da hukumar ta fitar a birnin tarayya Abuja kan yanayin da za a fuskanta.
Sai dai sanarwar ta ce wasu daga cikin jihohin na Arewa da suka hadar da Borno da Yobe, za a dan samu saukin hazon.
Haka zalika rahoton ya ce za a fuskanci rana a jihohin kudu da suka hadar da Cross River da Akwa Ibom, yayin da za a samu tsawa da yayyafi a jihohin Ondo, Ogun, Lagos, Edo, Bayelsa, Rivers, Delta.
You must be logged in to post a comment Login