Connect with us

Ƙetare

Hukumomi Jamhuriyyar Benin sun daƙile yunƙurin juyin mulki

Published

on

Ministan harkokin cikin gida na Jamhuriyar Benin ya bayyana a gidan talabijin ɗin ƙasar domin sanar da cewa yunƙurin juyin mulkin da wasu sojoji suka yi bai yi nasara ba.

Wani rukunin sojojin ƙasar ƙarƙashin Laftanar Kanar Pascal Tigri ya sanar da hamɓare Shugaba Patrice Talon tare da dakatar da tsarin mulki a kafar talabijin ɗin.

“Da safiyar Lahadi, 7 ga watan Disamban 2025, wasu tsurarin sojoji sun yi yunƙurin ƙwace mulki domin tayar da fitina a ƙasa da kuma ma’aikatu,” a cewar Minista Alassane Seidou.

“Ganin wannan lamari, sai rundunar sojan Benin, kamar yadda suka sha rantsuwa, suka ci gaba da mara wa ƙasarsu baya. Matakin da suka ɗauka ya ba su damar shawo kan lamarin kuma suka daƙile yunƙurin.”

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!