Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumomin Habasha sun sanya dokar takaita zirga-zirga a yankin Amhara

Published

on

Hukumomi a kasar Habasha, sun sanya dokar takaita zirga-zirga a yankin Amhara, biyo bayan zanga-zangar nuna adawa da yunkurin wargaza sojojin yankin, da gwamnatin kasar ke shirin yi.

Rahotonni sun bayyana cewa, An gudanar da zanga-zanga a garuruwa da dama na yankin Amhara tun bayan da gwamnatin kassar ta sanar da shirin shigar da rundunonin soji da wasu jihohi suka kafa, cikin rundunar soja ko ‘yan sanda ta tarayya.

Firaminista Abiy Ahmed ya ce, An dauki matakin ne saboda hadin kan kasar Habasha, inda ya yi gargadin cewa za a dauki matakan tabbatar da doka a kan duk wanda yake adawa da matakin gwamnati.

Wadannan dakarun yankin sun haifar da cece-kuce a baya, musamman a yankin Tigray da aka dauki tsawon shekaru ana gwabzawa da su, inda wadanda ke aiki a Amhara suka ba da taimako ga sojojin tarayya amma ana zarginsu da cin zarafin bil adama.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!