Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Ilimantar da mata kamar ilimantar da al’umma ne- wani malamin addini

Published

on

An bayyana hakkin malami a kan dalibi da kuma hakkin dalibi a kan malami a matsayin wani babban abinda ya kamata kowace makaranta ta baiwa fifiko musamman ma makarantun Islamiyya.

Wannnan ya fito ne daga bakin wani malamin addinin musulunci da ke Hotoron Arewa, Malam Abdussalam Aliyu a jawabin da ya gabatar a wajen bikin saukar Al’Qurani da makarantar Dau’ul Huda, Islamiyya ta gudanar a unguwar Hotoron Arewa.

Malamin ya ce dole ne mazaje, musamman ma gidanta su jajirce wajen ganin mata sun samu ilimi, ta yadda zasu baiwa ‘ya’yansu tarbiyya mai kyau.

Da take jawabi, shugabar makarantar, Malama Aisha Sulaiman ta ce suna kokari sosai wajen ganin mata sun samu ilimin addinin musulunci musamman ma ilimin zamantakewar aure.

Wakilinmu Muhammad Lawan Rano ya ruwaito cewa, a yayin taron an baiwa dalibai maza da mata da suka hada matan aure 37 shaidar saukar karatun Al’qur’ani mai girma.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!