Connect with us

Ƙetare

Ina da yaƙinin samar da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza- Trump

Published

on

Shugaban Amurka Donald Trump, ya ce, ya na da yaƙinin samar da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza.

 

Shugaba Donald Trump, ya bayyana hakan ne a ganawarsa da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a Litinin din makon nan.

 

Masu shiga tsakani sun ce, a lokacin ganawar ne Netanyahu ya kira Firaministan Qatar Mohammed bin Abdulrahman bin Jassim Al Thani daga fadar White House na gwamnatin Amurka, inda ya nemi afuwa kan hare-haren da ya ƙaddamar a ƙasar kan masu shiga tsakani na Hamas.

 

Ana ganin dai wannan na cikin tsare-tsare guda 21 da Amurka ta tsara, waɗanda Netanyahu ya ce, suna yin nazari a kansu.

Ana tunanin daga ciki akwai janye sojojin Isra’ila daga yankunan da ta mamaye, sannan Isra’ila ta amince da ƙasar Falasɗinu, ita kuma Hamas ta sako waɗanda ta yi garukuwa da su a cikin kwana biyu ba tare da illa ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!