Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kowane Gauta

Muna neman afuwar ‘yan Najeriyar da suka tallata APC – Magaji Yalawa

Published

on

Dattijo Magaji Yalawa ya nemi afuwar wadanda suka yi tallan jam’iyyar APC suka kuma zaba, saboda gwamnatin shugaba Buhari ta gaza karara.

Magaji Yalawa ya bayyana hakan ne ta cikin shirin Kowane Gauta na gidan Radio Freedom, yana mai cewa a cikin kaso dari na masoyan Buhari a yanzu bai fi kaso biyar ya rage ba domin duk sun dawo daga rakiyar gwamnatin sa.

Dattijo Magaji ya kara da cewa ‘yan Najeriya sun yi imanin idan gwamnatin Shugaba Buhari ta hau zata kawo sauyi mai kyau ga ‘yan kasa, amma sai suka fuskanci babu wani sauki da za su iya samu a gwamnatin Buhari.

Yace duk irin alkawuran da suka yiwa mutane musamman na yaki da ‘yan ta’adda da fashi da makami musamman a lokacin yakin neman zabe, gwamnatin Buhari ta gaza cimma wannan nasarorin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!